Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya kai ziyarar ta’aziyya ga Alhani Sanusi Maikano wanda wasu ‘yan ta’adda suka sace dansa mai suna Usman dan shekara takwas kuma suka kashe shi.

 

Yayin ziyarar ta’aziyar, Gwamna Tambuwal ya bayyana jimamin sa kan faruwar wannan aika-aika, inda ya bayyana cewa ya bada dama ga ja’mian tsaro da su tsaurara bincike domin gano wadanda suka aikata wannan mummunan aiki.

 

Gwamnan ya roki Allah ya gafarta wa mamacin ya kuma baiwa iyaye da ‘yan uwan yaron juriyar wannan rashinsa.



© hutudole

Post a Comment

 
Top