Gwamnatin Tarayya ta bayyana yajin aiki na mako biyu da kungiyar Malaman Jami’o’i ke yi a matsayin haramtacce.

 

Ta zargi ASUU da kin bin ka’idodi kafin aiwatar da haka.

 

Ministan kwadago, Dakta Chris Ngige, ya ba da matsayin gwamnati a Abuja bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya a ranar Laraba.

 

Ya ce ASUU ba ta ba gwamnati ‘sanarwar tilas’ ba na kungiyar kafin ta fara yajin aikin.

 

A wani furuci kamar Shagube Ministan ya aikewa kungiyar inda yace Idan kun karÉ“i sabis kuma har yanzu kuna son a biya ku, Shin rashawa ce. Ko ko Wannan ba cin hanci ba ne? ”



© Abubakar Saddiq

Post a Comment

 
Top