Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya bayyana cewa hukuncin kotu ta bashi daman ya ziyarci garin Awe in da ake ajiye da abokin sa domin ya ga halin da yake ciki.

 

” Kotu ta ba mai martaba daman zuwa ko ina, ban ga dalilin da zai sa kuma wai a hana wani ziyartar sa ko kuma hana shi watayawa ba.

 

” Mu a jihar Kaduna muna daraja sarakunan mu matuka, saboda haka duk inda muka iske mutane masu daraja haka zamu girmama su.

 

Bayan awa hudu da El-Rufai yayi a garin Awe tare da Sanusi, batan sallar juma’a sai kuma suka dunguma tare da mahaifiyarsa da ‘ya’yan sa biyu zuwa filin jirgin Abuja domin tashi zuwa Ikko, jihar Legas.



© hutudole

Post a Comment

 
Top