Ma gidancin mai kimanin shekaru 44, a ranar litinin ya nemi da kotun sauraran kararraki dake legas, data kashe auransu bisa zargin daya kewa matarsa tana holewarta da wani jami’in dan sanda.

 

Wadda ake zargi mai suna Rashidat wacce suke da ya’ya’ har biyu a tsakani, inda ya kara da cewa “Naduba wayarta wani lokaci inda naga irin kalaman batsa da take a WhatsApp ita da wani.

 

Ya bayyana ya sha yi mata magana amma tana uwar shegu dashi, gashi Sam bata shigar mutunci tamkar ba matar aure ba, na sha yi mata fada akan haka, amma dan abokaina suna shiga tsakanin mu ne, a cewar magidancin a lokacin da ya ke shaidawa kotu.

 

Itama ta tofa nata korafin a gaban alkali inda ta bayyana mijin nata a matsayin rigimamme, takara da cewa Mijin nata mai suna Ahmad yana yawan dukanta wanda bisa hakan yasa har sai da tayi bari sau biyu, ta kuma ce yanzu bata ma iya gani sosai saboda yawan dukan da yake yi mata.

 

Wanda hakan yasa take nemawa kanta mafuta.



© Abubakar Saddiq

Post a Comment

 
Top