Wadanda ake zargi da masu satar mutane ne a ranar Litinin da daddare sun sace daliban Rufus Giwa Polytechnic guda hudu a kan hanyarsu ta zuwa jihar Zamfara don halatar taron wayar da kai ga masu yiwa kasa hidma (NYSC) Wanda zai gudana a ranar talata.

 

Wadanda lamarin ya rutsa da su sun hada da maza uku da wata mata an sace sune a kusa da Funtua a cikin jihar Katsina da misalin karfe 11:30 na dare inda masu garkuwa da mutane dauke da makamai suka yi garkuwa da su a kan hanya.

 

Sakamakon wannan matakin, jami’an tsaro sun bada shawararsu ga masu ababen hawa don gujewa tafiye-tafiye a cikin dare musamman a wuraren da akwai barazanar tsaro.



© Abubakar Saddiq

Post a Comment

 
Top