Ma’aikatar lafiyar Faransa ta ce annobar murar Coronavirus ta halaka mutane 108 a kasar cikin kwana daya, adadi mafi muni tun bayan bullar da cutar tayi a kasar, bayan yaduwa daga China, gami da zamewa duniya annoba.

 

Alkalumma dai na nuni da cewa karfin yaduwar annobar karuwa yake a Faransa da sauran sassan nahiyar Turai musamman a Italiya inda lamarin ya fi muni, sai kuma Iran a yankin gabas ta tsakiya, inda annobar ta halaka mutane 149 a kwana daya.

 

A ranar laraba dai mutane 89 annobar murar ta Coronavirus ta halaka a Faransa.

Alakalumman baya bayan nan da hukumomin lafiya suka fitar sun nuna cewar idan aka dauke Italiya, kasashen Spain da Faransa ke kan gaba wajen fama da annobar murar ta Coronavirus a Turai, nahiyar da majalisar dinkin duniya ta bayyana a matsayin sabuwar cibiyar annobar.



© hutudole

Post a Comment

 
Top