Bayan da wani ya saka hotunan hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad na da dana yanzu, lamarin ya dauki hankula inda har bashir din ya mayar da martani.

 

Abin ya farune a shafin Twitter inda mutumin ya saka hotunan tare da musu taken, #Sakamakon Chanji, Mungode Baba Buhari”

Bashir ya bayyana cewa an dauki hoto na farko ne a shekarar 2006 yayin da hoto na 2 aka daukeshi s shekarar 2020. Yace banbancin wancan lokaci da yanzu shine ilimin da ya samu. Yace duk da cewa an taba hotunan(watau an musu kwaskwarima)amma ya amince dasu. Saidai ya shawarci wanda ya saka hotunan da ya koma makaranta ya nemi ilimi dan ba zai so ganinshi a shekarar 2030 yana irin wannan abu ba.

 

 

 



© hutudole

Post a Comment

 
Top