![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgqSFX2gnI_4xlVNWgPnybJsdJFEP_MO_J0g9BWrBKzGt3rx9AcYxum24Apx4_bCrJb4m8NPZDLBTUj-hNWdm6LhyphenhyphenVsucXjjhcH4eszjVEft_hHYWsoMARs6z77YRjQqX_JKUMISPnGpucw/s1600/xUmar-Ganduje-702x336.jpg.pagespeed.ic.bEAf04QhKv.jpg)
Gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje ya godewa mutanen jihar Kano bisa dama da suka sake bashi ya jagoranci jihar a karo ta biyu.
Ganduje ya bayyana cewa mutanen jihar sunyi na’am ne da irin romon deimokradiyya da yake ta kwarara musu lungu-lungu, kwararo-kwararo shine ya sa suka ga yafi dacewa da ya shugabance su a jihar suka fito suka zabe shi.
Ya bayyana cewa lallai ba zai yi kasa-kasa ba wajen ganin ya sassaka wa dadanda suka zabe shi har da ma wadanda basu zabe shi ba sannan zai yi gwamnati ne na kowa da kowa.
Idan ba a manta ba a jiya ne a aka bayyana zaben gwamnan jihar Kano inda gwamna mai ci Abdullahi Ganduje ya yi nasara a zaben.
Ganduje ya samu kuri’u miliyan 1,033,695 inda ya ba abokin hamayyar sa na jam’iyyar PDP, Abba Yusuf ratar kuri’u 8000 da yan wani abu.
Wannan zabe dai an koka a kan sa cewa jami’an tsaro ba su yi adalci ba a zaben.
Premiumtimeshausa.
Post a Comment