Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Zeezee ta yi wani jawabi a shafinta na sada zumunta inda tace, daya daga cikin kalubalen da mutum ke fuskanta shine tarin makiya

Ta kara da cewa saidai makiyine kawai zai yi maka gyara a lokacin da ka aikata ba daidai ba.

Ummi tace amma matsalar shine idan aka tashi yin gyara sai a rika yiwa mutum ta yadda bazai dauka ba maimakon a yi cikin Nasiha.

Wasu mabiyan Ummin sun jawo hankalinta akan kayan data saka a wannan hoton inda sukace be dace ba ta daina.

Saidai ummi tace kayan nata basu sabawa shari'a ba in banda gashin kanta da ta bari a bude kuma tana samun babban mayafi ya rufeshi tsaf zata iyayin sallah a haka.

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top