Jarumar fim din hausa, Ummi Zeezee ta saka wannan hoton na tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan a shafinta na sada zumunta da muhawara, inda ta rubuta cewa shine gwarzonta kuma gwarzon dimokuradiyya a kasarnan, to saidai wannan abu ya jawo zazzafar muhawara tsakaninta da wasu mabiyanta, inda akayi musayar maganganu masu karfi, amma wadanda sukafi jan hankali sune, wani yayi kira ga Ummi cewa ta daine danganta kanta da Jonathan saboda ba musulmi bane kuma Allah zai iya tashinta dashi a ranar kiyama.

Ummi ta mayarmishi martani da cewa to indai Allah zai tasheda Jonathan saboda tana sonshi to shima Buhari da Osinbajo Allah zai tasheshi tunda dai soyayyace tasa ya daukoshi ya bashi mataimaki....


Haka kuma Ummi sunyi musayar kalamai da wani wanda shima ta mayarmishi da martanin cewa waishi buharin waye da baza'ayi maganarshiba?, itafa saita zagesu shi da buharin babu abunda ya dameta......".


Ga karin hotunan yanda musayar kalamai ya kasance a dandalin Ummi.

















Post a Comment

 
Top