Bayan da tauraron mawakin hausa, Nazir Ahmad, Sarkin wakar Sarkin Kano ya saka wannan hoton nashi a dandalinshi na sada zumuntar Instagram, hadimin gwamnan Kano, Abubakar Aminu Ibrahim, me baiwa gwamnan Shawara akan kafafen sadarwar zamani, ya cewa Nazir, ka ci amana amma.

Haka kuma hadimin gwamnan yaje shafinshi inda yace, Nazirun da bainshi ya fada cewa sai abinda Hajiya Balaraba( daya daga cikin 'ya'yan gwamnan Kano) tace. Har ya jawo hankulan wasu abokan aikin Nazir din ya tambayesu wa ya tuna lokacin?

Saidai har zuwa lokacin wannan rubutun, Nazir be mayar da martani ba.


Post a Comment

 
Top