Wani Malamin Makarantar Islamiyya mai suna Malam Hashiru Bala da ke cikin garin Jalingo a jihar Taraba ya yi sanadiyyar ajalin dalibinsa bayan da ya murde masa wuya har lahira.

Dalibin mai suna Mohammed Sudais mai shekaru 9 da haihuwa dan wani hamshakin dan kasuwa ne da ke zaune a garin Jalingo.
An fara neman Sudais ne a ranar Lahadin da ta gabata bayan ya fita sallar Magariba kuma rashin jin duriyar sa yasa iyayensa suka bazama nemansa inda a sakamakon haka ne wani abokin Sudais ya fadawa iyayen yadda Malamin Islamiyyarsu Malam Hashiru ya yi ta masa wasu tambayoyi da bincike kan inda Sudais ke zuwa kafin bacewarsa.

©Alummata

Post a Comment

 
Top