![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgxJdyjyIZvZoPXU7nei2KCVvyiZhpGr6PDocKMlXuHX8I6NR3aimUvxFvnUVirlymFe_7W9NXDgt-LFLYo6VQJD7gl86f8EC8-atcMszn8lqrKuNumJyvIgQ5eFIhZugZr0oTgd4P4z-Ca/s1600/xAbba-gida-gida-660x336.jpg.pagespeed.ic.N9PRc0_fbL.jpg)
Dan takaran gwamnan jihar Kano na jam’iyyar PDP Abba Yusuf ya roki magoya bayan sa da su yi hakuri a jira a kammala zaben jihar Kano da aka bayyana bai kammalu ba.
A cikin takarda da ya fitar wanda kakakin sa Sanusi Dawakin Tofa ya saka wa hannu, Abba ya bayyana cewa idan suka yi hakuri komai zai zo ya wuce.
” An san mu da hakuri. Mu ci gaba da yin haka in Allah ya yarda muna a sama ko bayan an kammala zaben. Sannan kuma magoya bayan mu su sani cewa PDP ce ke kan gaba a sakamakon da aka bayyana mune a kan gaba kuma inda ma za a sake zabukan dun wuraren da muke da karfi ne aka soke.
” Ina kira ga wuraren da aka samu wadannan matsaloli da za a sake zabe su fito kwansu da kwarkwata su zabi jam’iyyar PDP a zaben.
Post a Comment