Farfesa Fatima Mukhtar da ta bayyana sakamakon Zaben Jihar Katsina a garin Katsina, sakamakon ya nuna ratar kuri’u sama da 900,000 ne Jam’iyyar APC ta ba PDP a Zaben Shugaban Kasa da aka yi.

Buhari ya samu kuri’u 1,232,133 Inda Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP, ya samu kuri’u 308,056 kacal.
A lissafe Buhari ya bashi ratar kuri’u 924,077.

Sakamakon Zaben ya nuna cewa Buhari ya you nasara a duka kananan hukumomi 34 dake Jihar Katsina.

©Premiumtimeshausa.

Post a Comment

 
Top