Wannan wata yarinyace me suna, Masenengen Targbo daga sansanin 'yan gudun hijira a jihar Benue 'yar shekaru 10 da rahotanni suka bayyana cewa marainiyace da aka samu wani ya mata fyade kuma har ta yi ciki.

Rahoton yace yarinyar ta haihune a jiya, Litinin a babban asibitin jihar saidai ba'a samu wanda ya mata cikin ba sannan kuma an barta ba tare da kowa ba.

Wannan yasa wani dan jarida ya fito yake nema mata taimako dan ta samu kayan kula da kanta da jaririyarta.

Post a Comment

 
Top