Tauraron fina-finan Hausa kuma mawaki, Adam A. Zango ya saka hoton wata matar aure a shafinshi na Instagram inda ya bayyana yanda take gayawa matarshi maganganu akan cewa nanbada dadewa itama zata zama bazawara idan Zangone.

Adamun yace matarshi ba 'yar fim bace dan haka kada tsanar da aka mai ta shafeta, yayi gargadin cewa ya lura matar dake wannan magana matar aurece dan haka na kusa da ita su ja mata kunne idan ba haka ba, nan gaba zai fallasa maganganun batsa data yi sannan ya dauki mataki a hukumance.







©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top