Yaseen Auwal, Darakta ne kuma Shugaban Kamfanin Shirya Fina-Finai na UK Entertainment, a hirar da ya yi da Aminiya a makon jiya ya bayyana irin alakar da ke tsakaninsa da Rahama Sadau da dalilin da ya sa mutane suke ganin yana da zafin rai. Daraktan ya kuma bayyana kudirinsa na shirya fim a kan Boko Haram. Ga yadda tattaunawar ta kasance:

Wane ne Yassen Auwal?



Sunana Yaseen Auwal, an haife ni a Unguwar Sarari a Karamar Hukumar Dala da ke Jihar Kano.  A nan Dala na yi makarantar firamare da sakandare, daga baya na yi kwas din aikin jarida (Mass Communication) a Jami’ar Bayero  (BUK) da ke Kano.

Me ya ja hankalinka ka shiga harkar fim?




A gaskiya na dade da fara fim, na fara da matsayin jarumi ne, wato tun lokacin da kamfanin shirya fim na Sarauniya Film Production suke daukar fim dinsu da su jarumi Gagare, idan ban manta ba wajejen 1994 zuwa 1995 ke nan. Ka ga shekaru ne masu yawa. Daga baya sai na fara shirya fim a shekarar 2000, inda kuma a 2001 na fara ba da umarni.

A baya a gaskiya fitowata a fim ta kuruciya ce, tunda ba wani shekaru ne da ni ba. A lokacin shekarar 2000 kuma mun kara yin wayo sai ni da wadansu abokaina muka hada kudi muka fara shirya fim, da za mu yi fim na biyu ne na ce zan fara ba da umarni, kuma tunda ina bibiyar yadda ake daraktin, ina bin darakta Sidi Ishak Sidi tunda shi ne ya yi mana daraktan fim dinmu na farko da muka yi. Bayan na nemi shawararsa a kan ina so in fara bayar da umarni sai ya fada mini abubuwan da ya kamata in yi, daga nan na fara daraktin a shekarar 2001.

Idan an ambaci Kannywood wane abu ne yake fara zuwa maka rai?

Idan aka ambaci Kannywood farin ciki ne yake zuwa zuciyata, babu abin da zan ce sai godiyar Allah. Sannan idan aka ambaci Kannywood a ko’ina ne hankalina zai koma kai, ko karatu nake yi a kafafen sada zumunta (social media) idan na shiga ina ganin an rubuta Kannywood ko mene ne sai na tsaya na duba in ga me aka ce a kanmu. Ina son masana’antata, a nan nake sana’a, ina son ci gabanta sosai.

Zuwa yanzu wadanne matsaloli kake fuskanta musamman ma ta bangaren ba da umarni?

A gaskiya babu wata babbar matsala da zan ce ina fuskanta, domin duk abin da na sa a gaba zan yi shi nake yi, kuma ina samun nasara a kai.

Me za ka ce game da jita-jitar da ake yadawa cewa akwai soyayya a tsakaninka da jaruma Rahama Sadau?

Soyayya tsakanina da Rahama Sadau babu ko kadan. Ni na kawo Rahama Sadau Kannywood, ni na fara sa ta a fim, tun daga lokacin da na fara sa ta a fim muke da kyakkyawar alaka, har kawo yanzu kuma babu wani abu zan ce ta yi mini na rashin kyautatawa. Tana mutunta ni, tana ba ni daraja, ina zama da ita sosai. Muna zama mu yi shawara, don yanzu kafin in fara waya da kai ma na dade ina magana da ita ta waya, duk da cewa tana Saudiyya. Alakar da ke tsakaninmu mutane suke gani kamar soyayya ce a tsakaninmu, amma ba haka ba ne.

A cikin fina-finan da ka yi wanne ka fi so, kuma me ya sa?

Duk fim din da na yi daraktin to ina sonsa, saboda ba na yin fim sai na ji ina so labarin, sai na karanta labarin fim din, na ji kuma ina sonsa sai in yi shi. Amma fim ya samu daukaka wannan kuma daga Allah ne. Haka ne ni ma a cikin fina-finan da na yi wani fim din ya fi wani samun daukaka ko fin kasuwa.


Yaseen tare da Rahama da kuma Mawaqi Umar M. Shareef
Wane fim dinka ne ya fi ba ka wahala?

Idan har ka kalli fina-finan da nake ba da umarni, yawancinsu masu wahala ne, ba na daukar fim mai labari kawai wanda za a ce ‘Action and Cut’. Ina so in yi labarin da zan sha wahala, irin fim din da kafin a dauki fitowa daya ma sai an sha wahala. Misali fim dina mai suna ‘Mati A Zazzau’, a Bauchi muka dauki fim din, fim din ya hada jarumai masu yawa, ga labarin da wahala. Fim din ‘Wani Gari’ ma ya ba ni wahala. Wani lokaci mutane za su kalli fim ma su ga kamar bai bayar da wahala ba, amma a wurin daukarsa an sha wahala.

Wani abu ne na farin ciki ya faru da kai a Kannywood da ba za ka taba mantawa da shi ba?

A gaskiya ba zan ce ga shi ba. Saboda abubuwan da suk

®Aminiyahausa

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top