Tauraruwar me sayar da kayan mata, Jaruma ta baiwa tauraron fina-finan Hausa kuma mawaki, Adam A. Zango gudummuwar Naira dubu rai 500 a matsayin gudummuwar auren da zai yi kwanannan.

A sakon data fitar ta shafinta na dandalin sada zumunta, Jaruma ta bayyana cewa ba ita tafi kowa kudi ba a Najeriya amma takan yi iya bakin kokarinta wajan bayar da kyauta.

Adamun shima ya nuna godiyarshi inda yace shiyasa yace ce mata Oga.

Post a Comment

 
Top