Da farko zaki gyara kayan miyanki dukkan abinda kikeso albasa tumatir tattasa attarubu in kina son tafarnuwa ma zaki iya sawa, sai ki kai markade.

 

~Bayan an markado sai ki juyeshi a abin tatar koko to dama akwai kusa a kafe a bango sai ki maqaleshi a jikin kusar zakiga ruwan kayan miyan yana zubewa zakiga farin ruwane yake zuba baa jijigawa sbd in kika jijiga kayan miyanki zai fita amma hakan idan baki jijigaba sai ruwan tumatir din ya ragu ,to amfanin hakan zaisa ki rage lkcn dahuwa tare da tattalin makamashi,i dan kikaga ruwan ya ragu sosai sai ki juye a tukunya kisa wuta ki barshi yayai ta dahuwaa amma zaki diga mai kadan baifi cokali uku ko biyu ba ya danganta da yawan kayan miyan,to idan ya jima yana dahuwa kuma kina dan jujjuyawa sbd kada ya kama yayi kauri.

~To dama kin wanke kwalaben baman ki sai ki dakko tukunya kinzubasu a ciki ruwan yasha kansu sai kisa gishiri a ruwan daga nan ki barshi ya dan yi minti biyar yana tafasa sai ki dakko kwalbar kizuba kayan miyan ki rufe.

Akwai wata takarda a jikin murfin baman to kada ki cire ki jefar sai ki maidata jikin murfin ki rufe haka zakiyi tayi har kayan miyan ya qare sai ki dakko su ki sake murda murfin kwalbar ki qara rufeshi sai ki maidashi cikin wanan ruwan tafasashe ki barshi yadan tafasa da to duk iskar dake cijin kayan miyan nan zata fita.

To inshaa Allah kayan miyan nan ba abunda zaiyi har tsawon shekara, ki lura bayan kin fitar dashi daga ruwan zafin nan to ki lura da murfin zakiga ya loma ya fada ciki this means kayan miyan yayi ba iska a cikin kwalbar.


© Sirrinrikemiji

Post a Comment

 
Top