Dalibin Makaranta Ya Diraka Ma Wata Malama ‘Yar Bautar Kasa Ciki

Wani dalibi a wata karamar makarantar sakandire da aka sakaya sunanta a jihar Abiya ya dirkawa wata budurwa mai yiwa kasa hidama karkashin NYSC cikin shege.

Lamarin dai ya janyo cece kuce a makarantar ta yadda akai mai yiwa kasa hidamar har ya bari dan aji uku na karamar sakandire yayi kwance kwance ya dirka mata ciki.

Wasu da dama na ganin duba da yadda ‘yar yiwa kasa hidimar ta baiwa dalibin tazarar shekaru bai kamata ace ya bari hakan ya auku tsakaninsu ba, yayin da wasu ke tunanin ko barazana dalibin ya yiwa budurwa.

Ana dai cigaba da gudanar da bincike domin gano bakin zaren matsalar da yadda za a warware ta.

© ๐Ÿ‘‰ #ArewaPlaza

The post Dalibin Makaranta Ya Diraka Ma Wata Malama ‘Yar Bautar Kasa Ciki appeared first on ArewaFresh.com™.


©Arewafresh

Post a Comment

 
Top