Na  daya  yin  murmushi idan ka  kalli fuskar matarka.
Manzon Allah saw yace murmushinka a fuskar Dan uwanka sadaka ne.  Tirmiziy
Na biyu sunbatar mace idan zaka fita (kiss)
Nana Aisha tace MANZON ALLAH saw yana sunbatar matarsa idan zai fita. ABU Dauda
Na uku Amincewa da ita da rashin tuhumar  ta
Manzon Allah saw ya hana mutum ya dinka fadowa matansa da daddare,  kada  ya dinka bin diddiginsu da zargi. Muslum.
Na hudu yin sallar dare tare da iyali.
MANZON Allah saw yace Allah yaji kan mutumin da ya tashi da daddare yana sallah,  kuma ya tashi matarsa,  idan taki ya yayyafa ruwa a fuskarta ABU Dauda
Na biyar . Nuna damuwa da halin da matar mutum take ciki,  na rashin lafiya da bata kulawa a Wannan lokacin, kamar yadda Annabi saw yake nunawa iyalinsa.
Na shida ka fada mata kana kaunar ta domin taji dadi,  kamar yadda aka tambayi Annabi saw,  wa yafi so yace Aisha.
Na bakwai Girmama iyayenta da danginta da kawayanta,  kamar yadda Annabi saw yake yiwa kawayan Nana Khadijah bayan rasuwarta.
Na takwas,  yi mata godiya da yabawa akan girki da kwalliya, domin taji dadi.
Na tara,  kada ta kawo abinci ko abin sha ya kushe,  kamar yadda Annabi saw, baya kushe abinci,  idan yayi masa ya ci, idan baiyi masa ba ya barshi.
Na goma. Ya dinka yin hira da tattaunawa da iyalinsa,  da kuma bata damar fadar raayinta.  Kamar yadda Annabi saw yake bawa matansa.
Na sha daya,  lallashin mace idan ta shiga damuwa,  da kwantar mata da hankali idan ta shiga halin tsoro da firgici. Kamar yadda Annabi saw yake yiwa iyalansa.
Na sha biyu,  kau dakai daga kurakurai da tuno alkhairinta a lokacin da aka sami matsala. Kamar yadda Annabi saw ya koyar kuma ya nuna a  aikace,   yace :  kada mumini yaki mumina saboda wani halinta da baya so. Domin tana da wani kuma da yake  so. Muslum ya ruwaito
Na sha uku ya dinka kiranta da suna mai dadi kamar yadda Annabi saw,   yake kiran Aisha da Humaira ko kuma Aish ko Ayish.
Na sha hudu,  ya dinka yi mata tsafta da  kwalliya kamar  yadda shima yake so ya ganta.
Na sha biyar,  ya dinka taimaka mata aikin gida,  kamar yadda Annabi saw yake taimaka iyalansa.
Na sha shida, yin wasa da iyali,  kamar yadda Annabi yake yi kuma ya koyawa Jabir cewa idan ya auri budurwa zaiyi mata wasa itama tayi masa,  yayi mata dariya ita ma tayi masa. Bukhari da Muslum suka ruwaito .
Na sha bakwai,  yin wanka tare  da Iyali  kamar yadda Annabi saw yake yi.
Na sha takwas,  yi dinka kwanciya yana tada kai da cinyar matar sa , kamar yadda Manzon Allah saw yake yi, tare da Aisha ko tana cikin jinin al'ada.
Na sha Tara,  YA dinka bata abinci a bakinta da cokali ko da hannu,  kamar yadda aka fahinmta daga hadisin Bukhari da Muslum,  cewa ,  Allah zai baka lada har lomar da kake sanyawa a bakin matarka,  wasu malamai sun fassara cewa , ka ciyar da ita kuma ba bata a baki da hannunka, 
Na ashirin, Idan matar ka taci abinci ta rage,  ka dauka kaci ragowar,  za taji dadi. Kamar yadda Nana Aisha tace idan naci abinci,  Manzon Allah saw yana ci,  a inda na saka bakina,  haka idan na sha abin sha,  yakan sha ta inda na sha. Muslum ya ruwaito.

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top