A jiyane tauraruwar fina-finann Hausa, Rahama Sadau ta yi murnar zagayowar ranar Haihuwarta inda tace ta cika shekaru 26 kenab ta kuma taya kanta murna da fatan Alheri. Da dama 'yan uwa da abokan arziki sun tayata Murna.

Rahama ta wallafa wasu daga cikin sakkonnin tayata murna da aka yi a shafinta na Instagram inda wannan na sama yana daga ciki.

Da take godewa wanda ya aika mata sakon wanda suka dauki zazzafan hotonnan dake sama tare, ta kirashi da Boon, abinda daya daga cikin hakan ke nufi shine Saurayi.

Post a Comment

 
Top