Koyi Da Manzon Allah (S.A.W) Ya Sa Na Auri Matar Da Ta Girme Ni Da Shekaru 11’
Jarman Bakori, Santurakin Galadiman Katsina,Alhaji Halliru Sa’ad Malami
A wannan makon ne tawagar ’yan jarida ta tattauna da Jarman Bakori, San Turakin Galadiman Katsina, Alhaji Halliru Sa’ad Malami a kan kiriro guraban aikin yi ga jama’ar garin Malumfashi fiye da 300 ta hanyar kafa katafaren kamfanin sarrafa shinkafa, man gyada da kuma wajen yin gadaje da kujeri irin na zamani da takalma domin taimaka wa al’umma wajen rage masu zaman kashe wando da kuma samar masu da hanyoyin dogoro da kai.

Kodayake a cikin hirar ya bayyana muhimmancin jama’a su rika yi wa ’yan siyasar da suka zaba suka tura su wakilce su a matakai daban-daban hisabi don gano kamun ludayinsu, ya ce bai da alaka da siyasa, sai dai yana tare da su ’yan siyasa, amma bai da sha’awar tsayawa wani mukamin siyasa. Ya bukaci mutane su cire kwadayi, zarmiyya, fadanci da raina na gaba in har suna son hakar su ta cimma ruwa a rayuwa.
Kwararre a harkar gine-gine, fasahar kasuwanci da kuma kayan kawa, wanda aka haifa a shekara 1982, wanda ya yi karatunsa a Malumfashi, Funtuwa, Abuja, Amurka da Dubai, ya yi wa manema labarai karin haske a kan yadda aurensa da tsohuwar matar Gwamnan Jihar Taraba; Danbaba Suntai ya kasance da kuma dalilin da ya sa ya ja bakinsa ya yi shiru tun wancan lokacin sai yanzu ya bara.

TAMBAYA: Watanni biyar da suka gabata an yi ta magana a kan yadda ka auri matar tsohon Gwamnan Jihar Taraba, Marigayi Danbaba Suntai, Hajiya Hawwa, me ya ba ka karfin gwiwar aurenta?

ALHAJI HALLIRU SA’AD MALAMI: Na yi ta kokarin kauce wa ’yan jarida a wancan lokacin. A matsayina na Musulmi na yi imani da kaddara. Na yi koyi da Manzon Allah (S) a kan yadda ya auri Nana Khadija. Hawwa shekarunta 47, ni kuma 36 a tsakanin mu shekaru 11. Ba wata tazara ce a tsakaninmu ba. Idan muka ce muna aikata wani abu na addini, na yin wani abu da za ka yi wanda za a yi koyi da kai na addini ko na gaskiya, ba za ka yi shi da baki ba, za ka yi shi ne a aikace. Ka ga shi kuma Maulumfashi, wannan shi ne garin da nake. Za ka iya ganin komai da kanku. Mutane sun fadi maganganu kala-kala, wasu sun ce ma ni Kwamishina ne a Jihar Taraba. Ni dai ban taba aiki da Danbaba Suntai ba. Duk wadannan ba gaskiya ba ne. Ban taba rike wani mukamin siyasa ba a Taraba. Na ga Danbaba Suntai ne sau biyu a rayuwarta, a lokacin da yake Gwamna in ya zo gidan Malam Umaru Musa ’Yar’aduwa. Ba mu dade da shakuwa da Hawwa ba, sai maganar aure ta shiga tsakanin mu. Daga nan sai muka shaku tamkar ’yan’uwan juna. Ban yi shirin aure a tsakanin mu ba, amma sai Allah ya kaddara. A wancan lokacin na tsara cewa ba zan shiga cece-kuce a tsakani na da mutane ba. Na yanke shawarar ba zan yi magana ba, balle mai da martani ga surutan mutane. Abin da ya fi dacewa shi ne ka kame, ka yi hakuri. Sai ka yi magana a daidai lolacin da ya dace. Ina son in fada maka, an fadi abubuwa da yawa a kanmu, ni da Hawwa. Ina so ka sani ni dan kasuwa ne da mutane sama da 1700 ke cin abinci a karkashina. Na tabbatar ba kowane Gwamna ne ya samar wa mutane masu yawa haka hanyar cin abinci ba.
Na yanke shawarar auren Hawwa ne saboda na ba da misali, na zama wanda mutane za su yi koyi da ni. Bari in ba ka misali, a bambancin shekaru 11 da ke tsakanin mu da Hawwa, a lokacin da take shekara 21, ni kuma ina da shekara 10, a wannan lokacin babu yadda za a yi ta yi tunanin za ta auri mutum kamar ni. Sai dai Allah yana da hanyoyin da yake tabbatar da wasu abubuwan da ya bar wa kansa sani. Kalli abokaina da muka taso tare, mun yi makaranta tare. Allah ya nufi ya fito da ni daga cikin su ba don ina da wani abu da ya fi su ba, na yi imani da Allah, a lokaci guda shi yake tsara abubuwan da za su faru.

TAMBAYA: A baya ka ce, kana da burin samar wa mutane aikin yi, ta wace hanya auren da kuka yi da Hajiya Hawwa zai taimaka wajen tabbatar da wannan burin naka?

AMSA: Al’amarin aure ko na rayuwa, duk abin da ka ce ka bar wa Allah ya yi maka, ko mai daren dadewa zai tabbata. Hawwa tana da

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top