Masha ALLAH...

Yau Alhamis 14 November 2019

Kungiyar Izala tayi nasarar kaddamar da komitin gina jami'a mallakarta me suna As-Salaam International University (AIU) a garin Abuja

Ga sunayensu kamar haka:

*Prof. Umar Muh'd Labdo (Chairman Committee)
*Prof. Ibrahim Muh'd Saleh
(Vice Chairman Committee)
*Alh. Ahmad Ibrahim Lau
(Secretary)
*Prof. Kabir Musa Yusuf
*Prof. AbdulMumin Hassan R/Dadi
*Prof. Haruna A Birniwa
*Prof. Aliyu Muh'd Bunza
*Justice Musa Danladi
*Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo
*Sheikh Yakubu Musa Hassan Katsina
*Sheikh Dr. Muh'd Kabir Haruna Gombe
*Sheikh Dr. Abdullahi Saleh Pakistan
*Sheikh Dr. Ibrahim A R/Lemo
*Engr. Ashiru Babandede
*Alh. Aliyu Isma'il

Shugaban wannan kwamiti Prof. Umar Muhammad Labdo yace zasuyi iya iyawarsu wajen ganin wannan gagarumin aiki na alkhairi da aka dora musu ya tabbata da yardan ALLAH.

Wakilin shugaban majalisar dattawa sanata mal. Ibrahim Shekarau (sardaunan Kano) yayi matukar nuna farin cikinsa da kuma yace shi kansa shugaban majalisar dattawa Sanata Ahmad Lawal (Senate President) ya jinjina ma kungiyar Izala wajen irin yadda take tafiyar da tsare-tsarenta,kuma hakan cigan kasa da al'ummah ne.

Me martaba sarkin Hadejia Alh Dr. Adamu Abubakar Maje (CON) ya nuna farin cikinsa matukar gaske, wajen ganin wannan jami'a da kungiyar Izala zata gina a kasarsa za'ayi, hakan ba karamin nasara bace ga al'ummarsa da sauran jama'a baki daya.

Shima shugaban wannan taron Alh. Aminu Dantata yayi farin ciki da ALLAH Ya kawo lokacin da kungiyar Izala ta samu dama zata gina jami'a mallakarta, yace hakan cigabanmu ne da 'ya'yanmu harma da makota baki daya

Kuma ya tabbatar da cewa zasuyi duk me yuwuwa wajen ganin wannan aikin alkharin ya tabbata cikin yardan ALLAH.

DAGA HAMZASUNNAH

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top