munyi binciken cewa kashi tisiin bisa dari na mata na fama da wannan matsala kuma muna samon complain sosai akan wannan lalura saboda haka muka yanke shawarar taimaka yanuwa mata da yadda muke hada magungunan wannan matsalar indai akabita to insha Allah zaa rabu da infection kwata kwata da ikon Allah ga hanyoyin kamar haka.

1- A samu Saiwar Garafuni da Sassaken Magarya, sai a tafasa, idan ya dan huce sai mace ta dinga kama ruwa da shi.

Kullum sau daya.

 Yana maganin budewa da kaikayi.

2- A samu Garafuni da Sassaken Sanya sai a tafasa, mace ta dinga shan rabin kofi da safe, rabi da yamma. Ya na fitar da dattin mara da maganin farin ruwa mai wari.

3- A samu Furen Tumfafiya, sai a shanya ya bushe, a daka a dinga zubawa a cikin Nono a na sha.

Ya na magance matsalar ruwan infection.

4- A samu Lalle da Ganyen Magarya da Kanumfari, a hada waje daya a daka sannan a tafasa a zuba farin miski a ciki.

Idan ya dan huce sai ta shiga ciki ta zauna tsawon kamar minti goma.

 Yin haka yana maganin kaikayi da kuraje da budewa da dadewar gaba.

5- A samu Kabewa a dafa ta, bayan an dafa sai a tsame daga ruwa a jajjagata ko a birga, a zuba Madara ko Nono sannan a sa Zuma a sha.

 Wannan yana mganin rashin sha’awa da bushewa da rashin gamsuwa.

6- A dafa Zogale, idan ya dahu sai a murje shi ko a dama, a tace, a yi lemon juice da shi.

 Yana maganin fitar farin ruwa mai wari da cushewar mara kuma ya na kara ni’ima.

7- A samu Dan-Tamburawa da Albabunaj a tafasa a zuba Man Hulba a ciki.

 Sai ta dan tsuguna tururin ya dinga shigarta.

Idan ya dan huce kuma sai ta shiga ciki ta zauna.

Zai magance mata kaikayi da kuraje kuma ya na sa matsewa.

8- A samu Farar Albasa da Kanumfari da Citta da Malmo da Barkono da Raihatul Hubbi, sai ta da ke su ta yi yaji ta dinga cin abinci da shi.

Ya na saukar da ni’ima da magance duk matasalolin sanyi.

9- A samu Sabulun Zaitun da Sabulun Habba sai a daka su. A samu ganyen Magarya da Garin Bagaruwa a daka a tankade.

Sai a zuba akan sabulan da aka daka sannan a kwaba da Ma’ul Khal, a zuba Man Tafarnuwa da Farin Almiski.

Sai mace ta dinga kama ruwa da shi kullum sau daya. Da ruwan dumi amma ake tsarki da shi.

 Wannan Sabulu ya na maganin kuraje da kaikayi da fitar wari.

10- A samu Man Zaitun da Man Habba da Man Tafarnuwa da Man Kanumfari sai a hade su waje daya.

 Mace ta dinga shan cokali daya kullum kafin ta karya. Ya na wanke dattin mara kuma ya na samar da ni’ima.

11- A samu Ciyawar Kashe-Zaki da Farin Magani sai ta hada waje daya ta dinga jika rabin karamin cokali ta na sha.

 Sannan ta dinga shan Man Zaitun Cokali daya kullum kafin ta karya. Wannan ya na maganin dattin mara da wanke daudar mahaifa.

12- A bare tafarnuwa, idan za ki kwanta bacci sai ki dauki sala daya ki yi matsi dashi, ana son idan mace za ta yi wannan hadin to miji ya daga mata kafa wato kada ya kusance ta, Da safe sai ta tafasa garin hulba ta zauna a ciki zata yi hakan har tsawon kwana uku.

13- Ki hada hulba da bagaruwa guri daya, ki dafa idan ruwan ya sha iska sai ki zauna a ciki, kuma ki samu man habbatussauda ki yi matsi da shi.

Ga wadanda basa iya hadawa tabbas munada hadaddun mugunan insha Allah kuma

Sai ku tuntubi shafin jima'i a koyarwa sunnah a facebook

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top