IDAN HAKA TA FARU DASU HAR KUKA SUKEYI

"Ni Karatu Zanyi Ba Aure Ne a Gabana Ba!

yayin da kaje neman auren mace yar shekara 18+ mafi yawa daga cikinsu haka zasu fada maka

idan kuma yarinya ta nuna tanada ra'ayin auren sai abata shawara da cewa" karatun nan shine gatanta, Haka zasuyita zugata!!

wai idan batayi karatu ba zata zama ci ma zaune, kome sai ta jira mijinta yayi mata ko ace mata idan mijinta ya saketa ko kuma ya mutu zata samu aikin gwamnati har ta dogara da kanta, sabo da kawai tunaninsu kaine zaka Rigasu mutuwa!!

yayin da ta gama karatun kuma lokacin takai shekara 23 ko 25 lokacin kuma sai burinta ya karu saboda tana jin kanta ita wata shegiya ce mai babban matsayin samun shedar Diploma, N.C.E ko kuma Degree Hakafa!!

ita bazatai aure ba sai irin mijin da ta tsarawa kanta zata aura,,, yan samarin da take kulawa abaya yanzu likafa taci gaba sbd haka ta renasu, to Ai shikenan muje zuwa!

samari kala-kala sunata zuwa wajenta amma ta tsaya ruwan ido ita sai mai kaza-da-kaza mai hannu da shuni bata auren talaka sai mai Money Hhhhh 

haka dai zata ci gaba da kasancewa har takai shekara 28 zuwa 30 ko 35 hahaha daga lokacin kuma samarin zasu fara tafiya suna guduwa domin ta fara tsufa wayyo Allah!!

ana cikin wanga hali sai kuma bukatar auren ta kamata sosai ba zato ba tsammani, sbd lokacin kawayenta duk sun hayyafa sun samu zuriya sosai , kwarai kuwa!!

daga nan sai kuma ta fara shiga malamai dan neman addu'ar samun miji koda ace tsoho ne sa'an babanta zata aura hhhh Abu yafara cin tura kenan!!

zata fara sayen alewa tana rabawa yara, ita kuma ta koma makarantar matan aure da neman sa'ar ko wani malamin zai aureta daga ckn malaman makarantar Isalamiyar da take zuwa!

haka dai abubuwan za suyita kasancewa amma idan Allah ya taimaketa sai kaga ta samu auren sa'an mahaifinta,,,kuma ba wai dan tana sanshi ba, saide dan kawai ta rasa mijin aure ne, wa yagaya miki Borno gabas take?

wata yarinyar kuma haka zataita zama ckn gidansu kullum da wando three quater domin taya mamanta aikin gida, Maganin me Ruwan ido kenan,

yayin da kuma wata zata fara tunanin zama matar kowa sbd sha'awarta koda yaushe motsawa take,,tana zuwa sharar office tana raba bonanza tana samun kudi amma hankalinta ba akwance yake ba

Dan Allah ku isar musu da wannan saqo

Gen Sunus Nasan A unguwarku A Akwai irin wadannan matan kagaya musu su kiyayi duniya tafi qarfinsu


© Sirrinrikemiji

Post a Comment

 
Top