Shigowar sanyi a mako biyu da suka gabata a nan Arewa ya sa Jaruma Rahama Sadau da Furodusa kuma Darakta Hassan Giggs sun tallafa wa almajirai da kayan sanyi a jihohin Kaduna kano,jaridar aminiyahausa na wallafa

Jarumar ta wallafa a shafinta na Instagram da Facebook cewa, “Mun zagaya jiya. Da dama daga cikin almajiran sun yi barci cikin natsuwa. Muna godiya ga wadanda suka bayar da gudunmawa. Allah Ya saka. Yanzu muka fara,” inji ta.

A makon jiya ne jarumar ta wallafa a shafukan nata cewa tana neman tallafin kayan sanyi domin tallafa wa almajirai a karkashin Gidauniyar Ray of Hope, inda ta ce, “Bai kamata a yi watsi da almajiran ba. Iska daya muke shaka. Ya kamata mu hada hannu wajen taimakon almajiran nan fisabilillah. Mu taimaka musu da riguna a wannan lokaci. Ina bukatar mutum shida: Ali Jita da Hadiza Gabon da Adam A. Zango da Umar M. Shareef da Sadik Sani Sadik su yi amfani da damarsu wajen isar da sakon nan kuma su taimaka. Kai ma za ka iya neman abokinka ya taimaka wajen bayar da gudunmawa ko yada bukatar nan.”

A Jihar Kano, Hassan Giggs ya kai wa amajiran daukin kayan sanyi domin samun saukin sanyin da ya kunno kai a kwanakin da suka wuce.

Hassan Giggs ya raba kayan ne a makarantun allo da dama a unguwanni da yawa na cikin birnin Kano.

ADVERTISEMENT
Hassan Giggs ya ce ya tallafa wa almajiran da kayan sanyin ne bayan ganin wadansu daga cikinsu da ya yi suna fama da matsanancin sanyi.

“Gaskiya kasancewar mun lura da yadda suke rayuwa cikin kunci  a wannan lokaci na sanyi, ya sa muka yi tunanin taimaka musu da kayan sanyin. Na lura cewa da yawansu ba su da kayan sakawa masu kyau, wasu ko takalma ba su da su. Idan ka auna za ka ga yaya mutum zai kasance ba tare da wadannan muhimman abubuwa ba.

Ya ce da ya lura da haka ne, sai ya kira abokinsa Ali Jita ya ce masa ya kamata su yi wani abu game da haka domin taimakon wadannan yaran da suke kwana a kan titi. Daga nan sai ya yi kira ga iyaye su dage wajen daukar nauyin da Allah Ya dora musu, sannan ya bukaci su saya wa yaransu duk abubuwan da suke bukata kafin su tura su makarantu.

Sai dai bayar da tallafin ya jawo cece-ku-ce a dandalin sada zumunta na facebook da Instagram inda wadansu suke yabo wadansu kuma suke suka, musamman ga Rahama Sadau. Aminiya ta tattaro wasu daga ciki kamar haka:

A shafin Facebook wani mai suna Muhd Al-ameen Drn cewa ya yi kan Rahama Sadau: “Alhamdulillah kan kirkiro wannan shiri. Wannan babban kalubale ga mutane musamman masu dukiya saboda kowane mutum yana da dama, kuma yana da kyau gare shi ya taimaki talakawa. Ina yi miki addu’a Allah Ya sanya wannan shiri ya zamo hanyarki ta zuwa Aljanna.”

Shi kuwa Sabiu Hussaini cewa ya yi: “Masha Allah alhamdulillah, Allah Ya kara karfafa miki gwiwa ki ci gaba da aikin alheri irin wannan na taimakon al’umma kuma Allah Ya kara daukaka ki Ya rabaki da sharrin makiya da mahassada, Rahama Sadau ikon Allah!”

Shi kuwa Kwamared Shafeeu Bello Idris Kaura-Namoda cewa ya yi cikin Ingilishi: “Mun gode miki. Kin yi aikin kwarai. To amma ki tuna ya kamata ki yi aure tare da kauce wa duk abin da ba ya da kyau kamar bayyana hotunan surar jikinki da sauransu. Allah Ya yi miki rahama ke da sauransu.. Allahummah Yashfeekee. ’Yar uwa”

Sai Agt Rabiaturraayi Rabiu Sakafa Malam Abdullahi Yahaya da Malam Sirajo Ladan suka ce: “Abin jin dadi! A lokacin da wadansu suke suka da watsi da tsarin almajirancinmu, sai ga wadansu suna kokarin tallafa musu. ALLAH YA ALBARKACI RAYUWANKI @Sadau”

Shi kuwa Abubakar Mustapha Kiru cewa ya yi: “Masha Allah! Wannan babban taimako ne. Sun cancanci a nuna musu soyayya da kula a kuma girmama su. Za mu ci gaba ne kawai idan muka koyi bayar da tallafi ga wadansu. Godiya gare ki kan bullo da wannan muhimmin shiri. Kuma ina da tabbacin zai samu nasara, saboda hannunki hannun zinari ne, duk abin da kia taba zai yi albarka. Allah Ya albarkaci wannan shiri Ya daukaka shi.#Gracias #Sadauzhomeonthespotlight #almajirimutum

Sai Abdulmumin Ibrahim Jega da ya ce: “Ki ci gaba Sadau, bayaninki na yau ya yi matukar sanya min farin ci

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top