Yanzu-Yanzu:Mutane Goma Da Zasu Jagoranci Sulhu Tsakanin Sarki Sunusi Da Gwamna Ganduje.

Wasu Manyan Dattawan Arewa Sunkafa Wani Kwamiti Na mutum goma Da zasuyi Sulhu tsakanin Mai martaba Sarki Sunusi Da kuma Gwamnan jihar kano Abdullahi umar ganduje.

Kwamitin Zai yi aikine karkashin jagoranci tsohon shugaban kasa Janar Abdussalamu Abubakar .

Mutum goma Da Zasu jagoranci Sulhun sune:

1.Alhaji Adamu Fika (Wazirin Fika)

2.Janar Muhammadu Inuwa Wushishi

3.Farfesa Ibrahim Gambari.

4.Dr. Ummaru Mutallab.

5.Dakta Dalhatu Sarki Tafida.

6.Gwamna Kayode Fayemi (Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nigeria.

7.Gwamna Aminu Bello Masari (Dallatun Katsina, Matawallen Hausa)

8.Sheikh Shariff Ibrahim Saleh.

Sai kuma Tsohon shugaban kasa janar Abdussalamu Abubakar.

Kwamtin zaiyi Aiki Ne Don warware rikicin dake tsakanin Sunusi Da ganduje kuma kwamitin Yabayyana cewa tuni Har ya far tuntubar gwamnan Da kuma sarkin.

Wannan Na zuwane bayanda Sarkin Yakarbi Nadin da Gwamna yayi Ma Sarkin A matsayin shugaban majalissar Sarakuna jihar.

Kafinnnan dai dama kungiyar dattawan Arewa karkashin jagorancin Hakim baba Ahmed Tafara Sasancin.

Inda shugaban kungiyar Hakim baba Ahmad yace bai kamata suna dattawa Su zura ido akan rikicin Ba Da gudun tashin tashina.

 

ku duba asalin wannan posting din daga babban shafin mu Yanzu-Yanzu:Mutane Goma Da Zasu Jagoranci Sulhu Tsakanin Sarki Sunusi Da Gwamna Ganduje. mun dauko wannan posting din daga babban shafin mu wato ArewaFresh.com. ArewaFresh.com - No1√ Best Entertainment Site In Nigeria.


©Arewafresh

Post a Comment

 
Top