A daidai lokacin da ake ta koke-koken tabarbaerwa harkokin kasuwancin fina-finan Hausa, shi kuwa Furodusa Abubakar Bashir Maishadda ba ya tsoron kashe kudi wajen shirya fim a Masana’antar Kannywood.jarimar aminiya n ruwaito.

A bara, Maishadda ya shirya fina-finai da suka hada da Mariya da Kanwar Dubarudu da Mudajala da Hafeez da Sareena da Hauwa Kulu da kuma Wutar Kara, inda duka ya samu nasara, kuma mutane suka yi ta yabawa, musamman ganin yadda fina-finan suka kyatar kuma suka nishadantar.

Ana cikin haka ne kuma kwatsam, sai Furodusan ya bayyana a watan Disamban bara cewa zai shirya fim da bai taba shirya kamarsa ba, kuma wanda ba a taba shirya kamarsa a Masana’antar Kannywood ba.

Hakan ya jefa masu kallo da sha’awar fina-finan Hausa cikin zullumi da jiran ganin fim din, wanda zai fi sauran da ya shirya.

Tun lokacin da kasuwancin fim ya fara tabarbarewa, wanda ya tursasa forudusoshi da dama  daina shirya fina-finai, wadansu kuma suka ajiye fina-finansu suka ki fitar da su, wadansu suka rufe ido suna fitar da fina-finan nasu.


Sai dai wadansu suna tunanin ko ana mayar da kudin da ake kashewa a fina-finan yanzu ganin cewa a sinima kawai ake haska fim din da sauransu, amma ganin ana kashe makudan kudi wajen shirya fina-finan, amma Maishadda ya ce zai yi wanda ba a taba yi ba, sai masu kallon suka fara tsimaya.

Abubakar Bashir Maishadda ya ce tare da Furodusa Kabiru Jammaje ne za su shirya fim din mafi girma a tarihin Kannywood.

Ya ce duk fina-finan da ya shirya da kuma nasarorin da ya samu kamar sharar fage ya yi.

Fim din mai suna The Right Choice, wato ‘Zabin da Ya Dace’ an shirya kashe masa zunzurutun kudi Naira miliyan 35, kuma ya kunshi manyan jaruman Kannywood da Nollywood wato na Kudu da Arewa.

Daga cikin jaruman fim din akwai Sani Mu’azu da Segun Arinze da Sola Sobowale da Nancy E.Isime da Enyinna Nwigwe da Ali Nuhu da Abba El-Mustapha da Asabe Madaki da sauransu kuma Ali Nuhu ne Daraktan Fim din.

Da Aminiya ta tuntubi Abubakar  Maishadda don ji ta bakinsa a kan  abin da ya sa fim din zai zama daban, lura da yadda ake ta maganar fim din, sai ya ce, “Fim din The Right Choice zai zama daban ne domin shi ne fim na farko da aka dauko jaruman Nollywood da dama, inda aka yi hadaka sosai da su, sannan lura da yanayi da lokacin da aka dauka ana yin fim din da yadda aka tsara shi da ma’aikatan da aka sa da abubuwan da fim din ke tattare da su da kuma yadda aka kawata shi, ya sa fim din ya bambanta da duk wani fim na Kannywdood, tun daga kashe kudi da kawata shi da sauransu.”

Game da abin da ya sa fim din zai fi girma a Kannywood, shin saboda yawan jaruman ne ko kudin da aka kashe ko saboda sakon da yake dauke da shi? Sai Maishadda wanda ake yi lakabi da Man Habu ya ce duk abubuwan da aka lissafo suna daga cikin abubuwan da suka sa fim din zai zama daban kuma ya zamo wanda ya fi girma.

“Tun kafa Kannywood, ba a taba kashe kudi a fim kamar kudin da aka kasafta kashewa wa fim din The Right Choice ba. Akwai tarin jarumai da aka dauko daga Nollywood da Kannywood, sannan bayan kudin, akwai batun sakon da fim yake dauke da shi. Duk wani mai kallon fim a  Afirka ta Yamma zai ji dadin fim din sosai. Labarin ne a kan wata ’yar jarida da ta shiga tashin hankali, kuma babbar jarumar ’yar Kudu ce,” inji shi.

Da aka sake tambayarsa ko zai mayar da Naira miliyan 35 da ya kasafta kashewa a fim din, sai ya ce ai komai Allah kadai Ke tsarawa, “Sosai ma ina sa ran zan dawo da kudin har ma in samu ninkin-ba-ninki na riba. Ka san komai Allah ne Yake tsarawa. Kai dai iya naka shi ne ka yi tsari mai kyau, kuma ka yi bincike mai kyau. Amma ai Allah Ya riga Ya kaddara komai. Kuma cikin ikon Allah, muna sa ran ba ma dawo da kudin da muka kashe ba, da yardar Allah za mu samun ninkin riba,” inji Maishadda.

Fim din wanda yanzu haka an kammala daukar zagaye na farko, saura zagaye na biyu ana sa ran za a kaddamar da haska shi a watan Disamba mai zuwa ne a sinima wato nan da wata 10.

Daya daga cikin jaruman da suka taka rawa a fim din wadda kuma ita ce ta ja

©HausaLoaded

Post a Comment

 
Top