Karuwanci bal laifi Bane a Abuja – Kotu

Wata babbar kotu dake Abuja babban birnin tarayyar Nigeria ta bayyana cewa babu wata doka Da tahana yin karuwanci.

Mai Shari’a Zainab Nyako Tabayyana cewa a dokar Nigeria babu wata doka Da tahana yin karuwanci .

Wannan yabiyo bayan Kama wasu masu zaman kansu Da jami’n tsaro sukayi tare Da gurfanar dasu gaban kuliya.

Mai Shari’a Zainab Nyako tabayyana cewa matan Da aka Kama bisa wannan zargi kotu tawanke Su Sannan Kotun tayi Umurnin Biyansu Diyya Sakamakon Tsaresu Ba bisa ka’ida Ba.

Lauyan matan Da aka gabatar Babatunde Jacob ya bayyana cewa kawai an bata Ma wadanda ake zargin lokaci Ne.

Sana’ar karuwanci dai wani Al amarine Daya yadu a dukkan biranen kasar sannan kuma masana na ganin hakan zai iya zama matsala ga kasa mai yawan Jama’a kamar Nigeria.

 

ku duba asalin wannan posting din daga babban shafin mu Karuwanci bal laifi Bane a Abuja – Kotu mun dauko wannan posting din daga babban shafin mu wato ArewaFresh.com. ArewaFresh.com - No1√ Best Entertainment Site In Nigeria.


©Arewafresh

Post a Comment

 
Top