Jiya Asabar cikin birnin Kano, aka daura auren wata baiwar Allah, mai suffofin yan'aljanna. Mace ce mai ilimin boko matakin digiri, hadi da na addini.

Kun san yadda bikin ya kasance?

An yi Walima mata zalla babu gardi ko guda daya. Amarya ta yi shigar mutunci har da nikabi. Ba wai iya nan ba, sai da aka yi wa'azi mai ratsa jiki a wajen walimar. Sannan aka dan yi rawa kadan kamar yadda shari'a ta sahalewa mata suyi lokacin.

Rariya.

Post a Comment

 
Top